Ƙasar Afrika ta Kudu ta kama mutum 133 da ake shirin yin safararsu




 Ƙasar Afrika ta Kudu ta kama mutum 133 da ake shirin yin safararsu



Ƴan sanda a Lardin Limpopo a Afirka ta Kudu sun Kuɓutar da mutum 133 da ake zargin an yi safararsu.


Kafar yaɗa labarai ta SABC ta ruwaito cewa mutanen da suka haɗar da yara da manya an same sune cikin wasu ƙananan bas-bas guda 10.


Wannan ne karo na uku da irin haka ke faruwa tun ƙarshen makon da ya gabata.


A Ranar Lahadi ne hukumomi a Limpopo suka kama fiye da ƙananan yara 400 da aka shigar da su Zimbabwe ba tare da wani babba a tare da su ba.


Hukumomin Zimbabwe sun musanta rahoton inda suka ce yara 124 ne kaɗai.


Ƙungiyar Save the Children ita ma ta ƙaryata iƙirarin Afirka ta Kudu cewa an sato yaran ne inda ta ce ba wai an kasi su Afirka ta Kudu bane domin yin aikatau.

Post a Comment

0 Comments